Hausa
Sorah Al-Qalam ( The Pen )

Verses Number 52

ن وَالْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 1
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
مَا أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 2
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
وَإِنَّ لَكَ لأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 3
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
وَإِنَّكَ لَعَلَى خُلُقٍ عَظِيمٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 4
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 5
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
بِأَييِّكُمُ الْمَفْتُونُSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 6
Ga wanenku haukã take.
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِالْمُهْتَدِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
فَلا تُطِعِ الْمُكَذِّبِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 8
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
وَدُّوا لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 9
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
وَلا تُطِعْ كُلَّ حَلاَّفٍ مَّهِينٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 10
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
هَمَّازٍ مَّشَّاء بِنَمِيمٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 11
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
مَنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 12
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
عُتُلٍّ بَعْدَ ذَلِكَ زَنِيمٍSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 13
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 14
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
إِذَا تُتْلَى عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الأَوَّلِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
سَنَسِمُهُ عَلَى الْخُرْطُومِSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 16
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
وَلا يَسْتَثْنُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 18
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 20
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
فَتَنَادَوا مُصْبِحِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 21
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
أَنِ اغْدُوا عَلَى حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَارِمِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
فَانطَلَقُوا وَهُمْ يَتَخَافَتُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 23
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
أَن لّا يَدْخُلَنَّهَا الْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 24
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
وَغَدَوْا عَلَى حَرْدٍ قَادِرِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 25
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوا إِنَّا لَضَالُّونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 26
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 27
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلا تُسَبِّحُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
قَالُوا سُبْحَانَ رَبِّنَا إِنَّا كُنَّا ظَالِمِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 29
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَى بَعْضٍ يَتَلاوَمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 30
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
قَالُوا يَا وَيْلَنَا إِنَّا كُنَّا طَاغِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 31
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
عَسَى رَبُّنَا أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَا إِنَّا إِلَى رَبِّنَا رَاغِبُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
كَذَلِكَ الْعَذَابُ وَلَعَذَابُ الآخِرَةِ أَكْبَرُ لَوْ كَانُوا يَعْلَمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 33
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّاتِ النَّعِيمِSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 34
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
أَفَنَجْعَلُ الْمُسْلِمِينَ كَالْمُجْرِمِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 35
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 36
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
أَمْ لَكُمْ كِتَابٌ فِيهِ تَدْرُسُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 37
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 38
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
أَمْ لَكُمْ أَيْمَانٌ عَلَيْنَا بَالِغَةٌ إِلَى يَوْمِ الْقِيَامَةِ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
سَلْهُم أَيُّهُم بِذَلِكَ زَعِيمٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 40
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
أَمْ لَهُمْ شُرَكَاء فَلْيَأْتُوا بِشُرَكَائِهِمْ إِن كَانُوا صَادِقِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ فَلا يَسْتَطِيعُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ وَقَدْ كَانُوا يُدْعَوْنَ إِلَى السُّجُودِ وَهُمْ سَالِمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
فَذَرْنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَذَا الْحَدِيثِ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لا يَعْلَمُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
وَأُمْلِي لَهُمْ إِنَّ كَيْدِي مَتِينٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 45
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 47
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
فَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلا تَكُن كَصَاحِبِ الْحُوتِ إِذْ نَادَى وَهُوَ مَكْظُومٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
لَوْلا أَن تَدَارَكَهُ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِ لَنُبِذَ بِالْعَرَاء وَهُوَ مَذْمُومٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
فَاجْتَبَاهُ رَبُّهُ فَجَعَلَهُ مِنَ الصَّالِحِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 50
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
وَإِن يَكَادُ الَّذِينَ كَفَرُوا لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَارِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا الذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُ لَمَجْنُونٌSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
وَمَا هُوَ إِلاَّ ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَSorah Al-Qalam ( The Pen ) Verse Number 52
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.