Hausa
Sorah Al-Hijr ( The Rocky Tract )

Verses Number 99

الرَ تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ وَقُرْآنٍ مُّبِينٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 1
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
رُّبَمَا يَوَدُّ الَّذِينَ كَفَرُواْ لَوْ كَانُواْ مُسْلِمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 2
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
ذَرْهُمْ يَأْكُلُواْ وَيَتَمَتَّعُواْ وَيُلْهِهِمُ الأَمَلُ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 3
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلاَّ وَلَهَا كِتَابٌ مَّعْلُومٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 4
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
مَّا تَسْبِقُ مِنْ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسْتَأْخِرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 5
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
وَقَالُواْ يَا أَيُّهَا الَّذِي نُزِّلَ عَلَيْهِ الذِّكْرُ إِنَّكَ لَمَجْنُونٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 6
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
لَّوْ مَا تَأْتِينَا بِالْمَلائِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 7
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
مَا نُنَزِّلُ الْمَلائِكَةَ إِلاَّ بِالْحَقِّ وَمَا كَانُواْ إِذًا مُّنظَرِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 8
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
إِنَّا نَحْنُ نَزَّلْنَا الذِّكْرَ وَإِنَّا لَهُ لَحَافِظُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 9
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا مِن قَبْلِكَ فِي شِيَعِ الأَوَّلِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 10
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلاَّ كَانُواْ بِهِ يَسْتَهْزِؤُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 11
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
كَذَلِكَ نَسْلُكُهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 12
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
لاَ يُؤْمِنُونَ بِهِ وَقَدْ خَلَتْ سُنَّةُ الأَوَّلِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 13
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
وَلَوْ فَتَحْنَا عَلَيْهِم بَابًا مِّنَ السَّمَاء فَظَلُّواْ فِيهِ يَعْرُجُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 14
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
لَقَالُواْ إِنَّمَا سُكِّرَتْ أَبْصَارُنَا بَلْ نَحْنُ قَوْمٌ مَّسْحُورُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 15
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
وَلَقَدْ جَعَلْنَا فِي السَّمَاء بُرُوجًا وَزَيَّنَّاهَا لِلنَّاظِرِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 16
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
وَحَفِظْنَاهَا مِن كُلِّ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 17
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
إِلاَّ مَنِ اسْتَرَقَ السَّمْعَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ مُّبِينٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 18
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
وَالأَرْضَ مَدَدْنَاهَا وَأَلْقَيْنَا فِيهَا رَوَاسِيَ وَأَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ شَيْءٍ مَّوْزُونٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 19
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
وَجَعَلْنَا لَكُمْ فِيهَا مَعَايِشَ وَمَن لَّسْتُمْ لَهُ بِرَازِقِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 20
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
وَإِن مِّن شَيْءٍ إِلاَّ عِندَنَا خَزَائِنُهُ وَمَا نُنَزِّلُهُ إِلاَّ بِقَدَرٍ مَّعْلُومٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 21
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
وَأَرْسَلْنَا الرِّيَاحَ لَوَاقِحَ فَأَنزَلْنَا مِنَ السَّمَاء مَاء فَأَسْقَيْنَاكُمُوهُ وَمَا أَنتُمْ لَهُ بِخَازِنِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 22
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
وَإِنَّا لَنَحْنُ نُحْيِي وَنُمِيتُ وَنَحْنُ الْوَارِثُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 23
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
وَلَقَدْ عَلِمْنَا الْمُسْتَقْدِمِينَ مِنكُمْ وَلَقَدْ عَلِمْنَا الْمُسْتَأْخِرِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 24
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
وَإِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَحْشُرُهُمْ إِنَّهُ حَكِيمٌ عَلِيمٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 25
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
وَلَقَدْ خَلَقْنَا الإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 26
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
وَالْجَانَّ خَلَقْنَاهُ مِن قَبْلُ مِن نَّارِ السَّمُومِSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 27
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
وَإِذْ قَالَ رَبُّكَ لِلْمَلائِكَةِ إِنِّي خَالِقٌ بَشَرًا مِّن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 28
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
فَإِذَا سَوَّيْتُهُ وَنَفَخْتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُ سَاجِدِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 29
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
فَسَجَدَ الْمَلائِكَةُ كُلُّهُمْ أَجْمَعُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 30
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
إِلاَّ إِبْلِيسَ أَبَى أَن يَكُونَ مَعَ السَّاجِدِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 31
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
قَالَ يَا إِبْلِيسُ مَا لَكَ أَلاَّ تَكُونَ مَعَ السَّاجِدِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 32
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
قَالَ لَمْ أَكُن لِّأَسْجُدَ لِبَشَرٍ خَلَقْتَهُ مِن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 33
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
قَالَ فَاخْرُجْ مِنْهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 34
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
وَإِنَّ عَلَيْكَ اللَّعْنَةَ إِلَى يَوْمِ الدِّينِSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 35
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
قَالَ رَبِّ فَأَنظِرْنِي إِلَى يَوْمِ يُبْعَثُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 36
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ الْمُنظَرِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 37
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
إِلَى يَوْمِ الْوَقْتِ الْمَعْلُومِSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 38
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
قَالَ رَبِّ بِمَا أَغْوَيْتَنِي لأُزَيِّنَنَّ لَهُمْ فِي الأَرْضِ وَلأُغْوِيَنَّهُمْ أَجْمَعِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 39
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
إِلاَّ عِبَادَكَ مِنْهُمُ الْمُخْلَصِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 40
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
قَالَ هَذَا صِرَاطٌ عَلَيَّ مُسْتَقِيمٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 41
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
إِنَّ عِبَادِي لَيْسَ لَكَ عَلَيْهِمْ سُلْطَانٌ إِلاَّ مَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْغَاوِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 42
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمَوْعِدُهُمْ أَجْمَعِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 43
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
لَهَا سَبْعَةُ أَبْوَابٍ لِّكُلِّ بَابٍ مِّنْهُمْ جُزْءٌ مَّقْسُومٌSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 44
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 45
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
ادْخُلُوهَا بِسَلامٍ آمِنِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 46
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
وَنَزَعْنَا مَا فِي صُدُورِهِم مِّنْ غِلٍّ إِخْوَانًا عَلَى سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 47
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
لاَ يَمَسُّهُمْ فِيهَا نَصَبٌ وَمَا هُم مِّنْهَا بِمُخْرَجِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 48
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
نَبِّىءْ عِبَادِي أَنِّي أَنَا الْغَفُورُ الرَّحِيمُSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 49
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
وَأَنَّ عَذَابِي هُوَ الْعَذَابُ الأَلِيمَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 50
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
وَنَبِّئْهُمْ عَن ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 51
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
إِذْ دَخَلُواْ عَلَيْهِ فَقَالُواْ سَلامًا قَالَ إِنَّا مِنكُمْ وَجِلُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 52
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
قَالُواْ لاَ تَوْجَلْ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلامٍ عَلِيمٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 53
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
قَالَ أَبَشَّرْتُمُونِي عَلَى أَن مَّسَّنِيَ الْكِبَرُ فَبِمَ تُبَشِّرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 54
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
قَالُواْ بَشَّرْنَاكَ بِالْحَقِّ فَلاَ تَكُن مِّنَ الْقَانِطِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 55
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
قَالَ وَمَن يَقْنَطُ مِن رَّحْمَةِ رَبِّهِ إِلاَّ الضَّالُّونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 56
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 57
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
قَالُواْ إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَى قَوْمٍ مُّجْرِمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 58
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
إِلاَّ آلَ لُوطٍ إِنَّا لَمُنَجُّوهُمْ أَجْمَعِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 59
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
إِلاَّ امْرَأَتَهُ قَدَّرْنَا إِنَّهَا لَمِنَ الْغَابِرِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 60
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
فَلَمَّا جَاءَ آلَ لُوطٍ الْمُرْسَلُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 61
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
قَالَ إِنَّكُمْ قَوْمٌ مُّنكَرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 62
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
قَالُواْ بَلْ جِئْنَاكَ بِمَا كَانُواْ فِيهِ يَمْتَرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 63
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
وَأَتَيْنَاكَ بِالْحَقِّ وَإِنَّا لَصَادِقُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 64
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
فَأَسْرِ بِأَهْلِكَ بِقِطْعٍ مِّنَ اللَّيْلِ وَاتَّبِعْ أَدْبَارَهُمْ وَلاَ يَلْتَفِتْ مِنكُمْ أَحَدٌ وَامْضُواْ حَيْثُ تُؤْمَرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 65
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
وَقَضَيْنَا إِلَيْهِ ذَلِكَ الأَمْرَ أَنَّ دَابِرَ هَؤُلاء مَقْطُوعٌ مُّصْبِحِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 66
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
وَجَاءَ أَهْلُ الْمَدِينَةِ يَسْتَبْشِرُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 67
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
قَالَ إِنَّ هَؤُلاء ضَيْفِي فَلاَ تَفْضَحُونِSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 68
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
وَاتَّقُوا اللَّهَ وَلاَ تُخْزُونِSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 69
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
قَالُوا أَوَلَمْ نَنْهَكَ عَنِ الْعَالَمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 70
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
قَالَ هَؤُلاء بَنَاتِي إِن كُنتُمْ فَاعِلِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 71
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
لَعَمْرُكَ إِنَّهُمْ لَفِي سَكْرَتِهِمْ يَعْمَهُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 72
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
فَأَخَذَتْهُمُ الصَّيْحَةُ مُشْرِقِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 73
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
فَجَعَلْنَا عَالِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن سِجِّيلٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 74
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَاتٍ لِّلْمُتَوَسِّمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 75
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٍ مُّقِيمٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 76
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً لِّلْمُؤْمِنِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 77
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
وَإِن كَانَ أَصْحَابُ الأَيْكَةِ لَظَالِمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 78
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
فَانتَقَمْنَا مِنْهُمْ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٍ مُّبِينٍSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 79
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
وَلَقَدْ كَذَّبَ أَصْحَابُ الحِجْرِ الْمُرْسَلِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 80
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
وَآتَيْنَاهُمْ آيَاتِنَا فَكَانُواْ عَنْهَا مُعْرِضِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 81
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
وَكَانُواْ يَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا آمِنِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 82
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
فَأَخَذَتْهُمُ الصَّيْحَةُ مُصْبِحِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 83
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
فَمَا أَغْنَى عَنْهُم مَّا كَانُواْ يَكْسِبُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 84
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
وَمَا خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا إِلاَّ بِالْحَقِّ وَإِنَّ السَّاعَةَ لآتِيَةٌ فَاصْفَحِ الصَّفْحَ الْجَمِيلَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 85
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ الْخَلاَّقُ الْعَلِيمُSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 86
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
وَلَقَدْ آتَيْنَاكَ سَبْعًا مِّنَ الْمَثَانِي وَالْقُرْآنَ الْعَظِيمَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 87
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
لاَ تَمُدَّنَّ عَيْنَيْكَ إِلَى مَا مَتَّعْنَا بِهِ أَزْوَاجًا مِّنْهُمْ وَلاَ تَحْزَنْ عَلَيْهِمْ وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِلْمُؤْمِنِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 88
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
وَقُلْ إِنِّي أَنَا النَّذِيرُ الْمُبِينُSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 89
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
كَمَا أَنزَلْنَا عَلَى المُقْتَسِمِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 90
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
الَّذِينَ جَعَلُوا الْقُرْآنَ عِضِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 91
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
فَوَرَبِّكَ لَنَسْأَلَنَّهُمْ أَجْمَعِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 92
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
عَمَّا كَانُوا يَعْمَلُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 93
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
فَاصْدَعْ بِمَا تُؤْمَرُ وَأَعْرِضْ عَنِ الْمُشْرِكِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 94
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
إِنَّا كَفَيْنَاكَ الْمُسْتَهْزِئِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 95
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
الَّذِينَ يَجْعَلُونَ مَعَ اللَّهِ إِلَهًا آخَرَ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 96
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
وَلَقَدْ نَعْلَمُ أَنَّكَ يَضِيقُ صَدْرُكَ بِمَا يَقُولُونَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 97
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَكُن مِّنَ السَّاجِدِينَSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 98
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
وَاعْبُدْ رَبَّكَ حَتَّى يَأْتِيَكَ الْيَقِينُSorah Al-Hijr ( The Rocky Tract ) Verse Number 99
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.